Abban Sojoji Takun Karshe Book 3 Chapter 110 (2024)

Abban Sojoji Takun Karshe Book 3 Chapter 110 (1)

Cikin natsuwa ta kammala sallar,zama tayi saman dardumar ta ɗaga hannayenta sama tana addu'a,kafin ta ƙarasa yin addu'ar Abu ta miƙe daga kan dardumar,saman gadon ta koma daga gefe ta zauna tana jan casbaha,

Tana cikin yin Addu'ar ta tunano da wannan malamin nasu na makarantar Boko Ya Mu'allim,tabbas suna buƙatar taimakon malamai domin magance waɗannan miyagun mutanan,Shafa addu'ar tayi kafin ta miƙe tare da ɗaukar sallayar ta nannaɗe ta,Cire hijab ɗin jikinta tayi ta mayar dasu a wardrobe,

Komawa tayi gefen oummansu ta zauna,

"Oumma"ta ambaci sunanta,

"Na'am?ba zaki koma bacci bane"?

"Zan koma,dama wata shawara nake nema a wurinki,me zai hana mu haɗa da malamai?su tayamu da addu'a,"

Jinjina kai Oummansu ta ɗan yi"Kinyi tunani mai kyau,yakamata mu sanya manyan malamai aciki,domin kawar da waɗannan Azzaluman mutanan da suka addabi rayuwarmu,mu ma kuma mu dage da addu'a,Allah dai ya kawo mana ƙarshensu kowa ya huta,"

"Ameen Oumma,"

Ta ambaci hakan tare da gyara kwanciyarta saman gadon ta kwanta,cikin lokaci ƙanƙani bacci yayi awon gaba da ita,dama jiya bata samu isasshen bacci ba,"

A 6angaren su Amrish kuwa,mommynta bata buɗe mata ƙopar ɗakinta ba,har sai wuraren ƙarfe takwas na safe,tana cikin taji mutsu mutsun za'a buɗe mata ƙopar,dama jiranta take yi,Saukowa tayi daga saman gadon ta tsaya ruƙe da qugunta tana jira a buɗe ƙopar,

Turo ƙopar Mommynta tayi hannunta ruƙe da key ɗin ɗakin,ganin Amrish tsaye a bakin ƙopar yasa ta ɗaure fuskarta"Lafiya kika wani ruƙe qugu kamar zaki dake ni"

"Mommy yanzu abunda kika yi mun kin kyauta!kamar wata dabba dabbar ma akuya haka kika rufe ni a ɗaki batare da kinyi tunanin wani abu zai iya faruwa dani ba?meyasa Mommy?wai laifin me na aikata maki ne"?ƙarasa maganar tayi yayin da idanuwanta suka cicciko da ƙwalla,

Ta6e baki mommyn tayi dama ba imani ta cika ba,

"Rashin jinki ne yasa nake rufe ki a ɗaki,kin cika bin ƙwaƙƙwafin tsiya shegen sa ido,ga taurin kai,Ban isa na faɗa maki abu ki yi ba,da ace kina respecting ɗina as ur mother,da mun zauna lafiya,"

"Shikenan Mommy in har wannan ne dalilin dayasa kike yi mun haka,Wlh zan daina......"

Katse mata hanzarinta tayi"Zaki daina!ko kin daina,ban fahimceki ba"?

Da sauri Amrish tace"Na daina,"

Jinjina kai Hajiya Sarat tayi"shikenan,Kin ga yanzu zamuyi zaman Lafiya dake,faɗamun me kikeso na kawo maki ki ci"?

Yatsina fuska Amrish tayi still bata yarda da mommynta ba,

"Duk abunda kikeso Mommy shi nake so,Yanzu dae dan Allah mommy wayata nakeso ki bani!pls mommy nayi missing ɗinta sosai,school friends ɗina duk nayi kewarsu,ina so nayi chatting dasu,"aɗan shagwa6e ta ƙarasa maganar,

"Amrish!ni kaina bansan inda na jefa wayarki ba acikin gidan nan,Ranar kin 6ata mun raine,shiyasa Na ɗauketa,but in kinaso Zamu fita shopping atare daga nan saiki za6i wayar da kikeso,"

Daƙyar Amrish ta ƙaƙaro murmushi akan fuskarta,

"Shikenan mommy,Yanzu bari na shiga ciki nayi brush,"

"Idan kin kammala brush din,Ki jira ni a dining,"ta ƙarasa maganar tare da juyawa ta sauko Downstairs,"

Komawa cikin ɗakin Amrish tayi,tsayawa ta ɗanyi ruƙe da qugu aranta tana faɗin"Matar nan bata da gaskiya,ko su waye suka shigo daren jiya?daga gani ba abun arziƙi suka aikata ba shiyasa suka garƙame ni acikin ɗakin kamar wani ɗan kuikuyo,"

Ƙwafa tayi tare da nufar toilet,ta shiga ciki,

After ta kammala,har wanka ta ɗanyi ta zura jeans da farar vest ajikinta,Saukowa downstairs tayi atsanake take tafiya,hannunta acikin aljihun wandonta irin nigogin nan,

Tana cikin tafiyar nan kwatsam taji ta taka wani abu a ƙafarta,da sauri ta ɗan ɗaga ƙafarta tare da kai idanuwanta kan abun,Wrist watch ce da alama yarda ta akayi a ƙasa,Zuƙunnawa tayi agaban agogon sai faman ƙyalli take yi da alama ta Diamond ce,

Hannu tasa ta ɗauki agogon tana jujjuyata,Aranta tana ayyana farashin agogon,Daga gani ba ƙaramin diamond bane,Don tunda ake siya mata Diamond ba'a ta6a siya mata mai ƙyalli kalar wannan ba,Agogon ta haɗu sosai,Tayi mata kyau,

Murmushi ta saki tare cewa"Yanzu haka cikin baƙin jiya ne da suka shigo cikin gidan nan da daddare aka samu wani ya yarda ita ƙasa wanda baisan muhimmancin kuɗinshi ba,Ko kuma wanda bada guminshi aka siya agogon ba,"

Jin takun takalmin Mommynta Yasa tayi saurin,zura agogon acikin aljihun jeans ɗin jikinta

"Wlh bazan bari mommy taga wannan danƙareriyar agogon ba,Don ta burgeni da ita Zanyi Hotunan Birthday ɗina,Inyaso daga baya sai a mayarwa mai agogon kayanshi,"

Ta ƙarasa zancen zucin tare da miƙewa ta wuce dining,Kujera taja ta zauna tana jiran ƙarasowar breakfast ɗinta,

Shigowa area ɗin Hajiya Sarat tayi hannunta ruƙe da faffaɗan tray mai ɗauke da kayan kalacinsu,Saman table ɗin ta ajiye tray ɗin,

Murmushi Amrish ta saki tare da yi mata sannu"

"Yawwa Daughter,"ta amsa mata a yayin da take ɗaukar plate,warmer ta buɗe mai ɗauke da Chips ta soma zuba mata,bayan ta gama ta haɗa mata da kakkauran Tea,tare da slide bread wanda aka jerashi da wainar kwai,"

Nan fa suka hau cin abincin atare suna fira,abunda basu ta6a yi ba ita da amrish,

Wuraren ƙarfe 9,Sehrish ta farka daga bacci tana ta faman yin hamma wata irin matsiyaciyar Yunwa ce ta addabe ta,Saukowa tayi daga saman gadon babu kowa a ɗakin,duk sun fita yin breakfast,ita kaɗai ta rage,

Toilet ta shiga,shaf shaf tayi wanka after some minutes ta fito ɗaure da towel,gaban mirror ta zauna tana shafa mayukan jikinta,sai da ta kammala mulke ko'ina,Sannan ta ɗauki powder zata shafa,Kamar ance ta ɗago ta kalli mirror,kwatsam ba zato ba tsammani taga madubin ya koma mata tamkar tv,manya manyan bishiyoyi ta gani acikin daji ga wasu gwaggon burai gandara gandara masu uban gashi ajikinsu,Sae miƙo mata hannu suke yi ta cikin madubin suna kiran Sunanta"Sehrish kizo,Sehrish kizo"shi ne abunda suke faɗi

Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu,Idanuwanta suka firfito waje tamkar ƙwayar idonta zata faɗo ƙasa sai kuma taga madubin ya koma lafiya lau,jikinta na kerma ta miƙe ta bar gaban madubin,Da sauri da sauri ta buɗe wadrobe ta ɗauko jallabiya ta zura ajikinta,Mayafin ma a hannu ta ruƙe shi,ko takalmi bata sanya a ƙafarta ba,Gudu gudu sauri sauri ta fito daga cikin ɗakin,

Lokacin da ta ƙaraso dining area din gaba ɗaya ta samu kowa zaune suna cin breakfast ɗinsu,tun daga kan Daddynsu Abusufyan,Oummansu da kuma su Hosana da Jahad,Ga Abba kuma tare da Mommynsu Alex,sai su twins da fawan kanal yousouf dasu Jabeer,Ganin Azmee tayi atsaye tana yin serving ɗinsu,Nan fa ta ƙara shan jinin jikinta,

Jiki asanyaye ta ƙarasa dining ɗin,hankalin kowa ya dawo kanta,

Fuskarta ɗauke da murmushi ta soma gaisar dasu"Abba ina kwana"

"Lafiya lou ƴan matan Abusufyan"murmushi ta ɗan saki tare da kallon Mommy"ina kwana mommy an tashi lafiya,

"Lapiya lou Daughter,"

Komawa tayi kan Daddynsu"Ina kwana daddy kun tashi lafiya,"

Fuskarshi ɗauke da murmushi Ya amsa mata"lafiya lou daughter,An sha bacci ko"?

Dariya sehrish ta ɗan yi tare da kallon Oummansu ta gaisar da ita,Sai da tabi kowa ta gaisar dashi,tana ƙoƙarin zama Abusufyan yace'baki ga Aunty Azmee bane?naga kamar baki gaisar da ita ba,"

Jimm ta ɗanyi kafin ta wurga eye balls ɗinta kan fuskar Azmee dake tsaye,murmushi ta samu akan fuskarta,

Ba don taso ba hakanan ta daure ta gaisar da ita"ina kwana Aunty Azmee,"

"Lafiya lou Sehrish,Yanzun nan nake shirin zuwa na taso ki sai gashi ma kin fito"

Baki asake Abu da sehrish ke kallonta,Ta ƙware wurin iya kisisina da munafurci,

Banza sehrish tayi,batare da ta tanka mata ba,

Zagayowa Azmee tayi wurinta tare da kai hannu ta ɗauki plate,Warmer ta buɗe mai ɗauke da farfesun Ƴan cikin shanu,Ta zuba ma Sehrish ta tura mata shi agabanta,

Zuƙunnawa tayi daidai saitin kunnan sehrish cikin raɗa tace"Nasan zaki ji daɗin shan farfesun nan,"

Tana kai ƙarshen maganar ta miƙe daga tsaye,kallon Oummansu tayi da ido tayi mata alamar ta kwantar da hankalinta,

Ajiyar zuciya ta ɗan sauke tare da zura yatsun hannunta cikin plate ɗin,A tsanake ta soma shan farfesun ba ƙaramin daɗi yayi mata ba,

Sai da ta nutsa cikin shan farfesun ta dinga jin motsin wani abu a hannunta,duk in takai hannu zata ɗebo ƴan cikin sai taji suna kufce mata daga hannunta kamar abu mai rai,hakan yasa takai idanuwanta cikin plate ɗin,Tsutsotsi ta gani suna yawo acikin plate ɗin manya manya,A wani irin firgice Sehrish tayi wurgi da plate ɗin ta fasa Uwar ƙara,Nan take ta shiga kwarara Amai,

Gaba ɗaya hankalin Kowannansu Ya tashi haiƙam,Mikewa tsaye su kayi suna kallonta,kowa na tambayar Lafiya,Da ƙarfi take ambaton Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Wayyo Allah na,Na bani na lalace Daddy,Oumma ku taimake ni,Naci tsutsotsi acikin cikina,

Tana magana amai na zuba daga bakinta,duk ya 6ata gaban rigarta jaga jaga,duk tabi ta gigice ta rikice,Watsa wa tayi da gudun gaske tana kuka ta nufi bedroom ɗinsu,A guje Suka bi bayanta

Toilet ta faɗa cikin fitar hayyaci ta nufi basin,Cigaba da kwarara aman tayi har saida takai ga babu abunda ke fitowa bakinta sai ɗigon jini ta ƙarar da koma da taci ko ruwa babu a cikinta,

Soso ta ɗauko tare da detergent ta zazzaga shi abakinta,Adai dai lokacin suka ƙaraso ƙopar toilet ɗin,sunyi ƙoƙarin su tura ƙopar amma ƙopar ta datse sakamakon Bugata da sehrish tayi bayan ta shiga,Ƙwanƙwasa ƙopar suka shiga yi kowa na ambaton sunanta,

'Sehrish!kizo ki buɗe mana ƙopa,kada ki Lahanta kanki fa,"muryar Oummansu ce keyi mata magana,tamkar zata fashe da kuka

Abusufyan ma murya na kerma yace"Wai baza ki buɗe mana ƙopa ba?meyake damunki ne?Dan Allah Daughter ki fito kiyi mana bayani,"

Kwata kwata Sehrish bata jinsu domin kuwa ta jima da makancewa,Ta fita hayyacinta,abunda ta gani a plate ɗinta keta dawo mata cikin kanta,

Tura soson tayi abakinta,Ta dinga gurzar bakin,har saida Le6enta suka faffashe jini ya soma zuba ta ko'ina abakinta,daga waje suka dinga jin Azababben kukan da Sehrish ke yi,na tashin hankali,

Da gudun gaske Abusufyan yabar ɗakin kaitsaye ya nufi upstairs don ya sanar da Sgr,Suzo su 6alle ƙopar kada ta kashe kanta,

Lokacin da ya shiga Part dinshi ko sallama babu,faɗawa kawai yayi gudu gudu sauri sauri ya shiga bedroom ɗinshi,Sai faman haki yake yi,A kwance ya sameshi yana bacci jikinshi sanye da jallabiya,

Tun kafin ma Ya ƙarasa wurin gadon ya shiga ƙwala mashi kira"Rafayet!Rafayet!!"

Farkawa Sgr yayi lokaci guda ya wurga idanuwanshi masu ɗauke da bacci kan Abusufyan dake ta kwala mashi kira,

"Uncle lafiya"?

"Ina fa lafiya!Ga sehrish can zata kashe kanta acikin toilet,bamu san meke damunta ba,sai ihu take tana kuka,Munyi munyi mu buɗe ƙopar ta datse ta,"

Tunkafin Ma Abusufyan yakai ƙarshen maganarshi,Sgr ya sauko daga saman gadon,da wani irin sauri ya fito daga part ɗin,gudu gudu sauri sauri Ya nufi bedroom ɗinsu,Abusufyan kuwa bai baro Upstairs ɗin ba sai da ya wuce ɗakin Omar ya taso shi daga baccin don abun kowa ta shafa,

Lokacin da Sgr ya ƙaraso ɗakin abun ya tashi hankalinshi sosai,Tunda ya shigo corridor ɗin ɗakin Ya fara jin sautin kukan da sehrish keyi,Tamkar ana zare ranta daga jikinta,

A sukwane ya faɗa cikin ɗakin,Ganinshi yasa suka matsa mashi daga wurin ƙopar,A zafafe ya daddage ya bangaji ƙopar da ƙafaɗarshi,Nan take ƙopar ta buɗe,Faɗawa cikin toilet ɗin yayi a lokacin Harta yanke jiki ta faɗi ƙasa,jinin da ya gani jaga jaga ajikin basin ɗin ba ƙaramin tayar mashi da hankali yayi ba,inda take kwance kasa ga soso nan a gefenta ga kuma ledar detergent ɗin da ta fasa,Bakinta yayi jaga jaga da jini fatar le6enta ta munana duk rauni,

Jikinshi Yayi mugun sanyi,yaso ace tun lokacin da ta fara haukan suka sanar dashi,slowly ya zuƙunna agabanta,tare da kai hannu ya tallabo kanta,da hannu ɗaya,Ɗayan hannun kuma zura shi yayi cikin bakinta Ya buɗe shi,runtse idanuwanshi yayi yayin da zuciyarshi ke ta faman tafarfasa,harshenta gaba ɗaya ya faffashe,detergent ɗin yayi mata illa sosai,duk ya sale fatar harshen nata,Yaji raɗaɗin abun har cikin zuciyarshi,miƙewa yayi azafafe ya juya yana kallonsu dayake duk sun shigo cikin toilet ɗin,Oummansu sai kuka takeyi,Haka su Jahad da Hosana ma,

"Tun yaushe ta fara wannan abun?meyasa ba'a sanar dashi ba!"a ruɗe yayi maganar

"Rafayet yanzu duk ba lokacin wannan bane dan Allah ka taimaka,kada mu rasata,"Abbansu Yayi maganar fuskarshi duk a hargitse

Juyawa yayi tare da sanya duka hannayenshi ya ɗaukota tare da ɗaurata saman kafadarshi,Ya fuce da ita daga ɗakin,A hanzarce Ya haura da ita Upstairs part ɗinshi,A saman gadonshi ya kwantar da ita,da sauri ya kuma saukowa down bayan ya ɗauki key Ya nufi medical Room ɗinsu,da kanshi Ya shiga duba Sehrish koda ta farfaɗo tana koke koke Allurar bacci yayi mata,

kowa ya shiga damuwa,abincin ma duk sun ƙoshi dashi,A ƙarshe saman Sofa kowa ya zauna cike da jimamin halin da Sehrish ta shiga,Abun ya ta6a masu zuciyarsu sosai,

Har lokacin abu bata daina kuka ba,Haka Jahad da Hosana ma

"Dan Allah ku kwantar da hankalinku,In sha Allah Sehrish zata samu lafiya,"acewar Kanal yousouf,

"Kusan kashe kanta tayi fa,Omo ta zuba abakinta ta wanke da soso,Ni bansan meke damunta ba,Sae faman ambaton tsutsa takeyi ni banga komai ba a plate ɗin abincinta,"Abusufyan ne yayi maganar idanunshi cike tab da kwalla,

"Dole akwai wani abun dake damunta,ni tsorona ma kada ta Zauce"

Abba da Mommy sai kwantar musu da hankali suke yi,

Hannun Abu sae kerma ya ke yi,acan ƙasan zuciyarta kuwa,tunanin yarda zata fallasa Azmee take yi don tasan cewa itace Silar Halin da Sehrish ke ciki,tayi jinkiri ne saboda bata jima da zuwa gidan ba,ba lallai bane su yarda da maganarta ba,

Miƙewa Tayi tare da kama hanyar zuwa kitchen,tana shiga ta samu Azmee tana gyara kitchen ɗin,hankalinta kwance,

"Meyasa kika yi mata haka"?ɗagowa Azmee tayi tare da kallon abu dake tsaye,lokaci guda ta saki murmushin gefen fuska tare da cewa"Bangane akan me kike magana ba"

"Amma baki da Imani!munaf*cka mai fuska biyu,kina son ki cutar da ita ne saboda kina tsoran karta tona maki asiri,shiyasa kike ƙoƙarin kashe mun ita"tana magana hawaye na zuba akan fuskarta,,

Girgiza kai azmee tayi"ko kusa ni bani da alaƙa da Abunda ya faru da Sehrish!kada kiyi mun ƙazafi,Ni bazan iya cutar da Sehrish ba,Saboda ina jinta tamkar ƴar cikina....."

Tunkan takai ƙarshen maganar a fusace abu tace"karki kuskura ki ƙara kwatanta sehrish da ƴar cikinki!mushirika kawai,muguwa kuma azzaluma!Makira!Ni bana jin tsoronki,Da Allah na dogara ba da wani tsubbace tsubbace ba irin naku,waɗanda suka jahilcewa addininsu,har yaushe ne zaku gane gaskiya ku daina aikata irin wannan mummunan zunubin da kuke aikatawa ne?Kuna ɗaukar kanku tamkar wasu shaggu saboda kawai kuna taƙama da tsafin da kuke dashi,In banda ma daƙiƙanci da jakkanci da jahilci irin naku,Kun manta cewa Allah shi ya halicce ku kuma a kowani lokaci zai iya ɗaukar ranku,Kuma zaku koma gareshi sannan ku gir6i abunda kuka shuka,akwai ranar da wannan sihirin da kuke taƙama dashi bazai ta6a amfanarku ba!tunda baku isa ko mutuwa ku hana kanku ba....."

Tunkan ta ƙarasa Maganar Azmee ta daka mata tsawa har sai da abu ta girgiza"Ya isa haka!ke baki isa ki ce zakiyi mun wa'azi ba!Idan ilimin addini kike taƙama dashi,ko ƙafata baki kama ba!ke kinsani basai na faɗa maki ba,Idan da naso tun lokacin dana zo gidanki yi maki wankan jego da tun lokacin Na murƙushe ki ke da ƴa'ƴan naki,Amma banyi hakan ba don baki acikin ainihin abun hari na,Idan har kika cika zaƙewa Wlh Zaki rasa Rayuwarki ne!Zanyi silar da zaki bar duniyar nan ne!

"Raina ba ahannunki yake ba!A hannun Allah yake,Idan har kinga na mutu to lokacina ne yayi,kuma koda ace Na mutu ta silarki,inaso ki sani kema wata rana zaki zo inda nake ne,kuma zaki yi bayani ne,banza kawai,ina ilimin da kike taƙama dashi ne?ai dake da dabba duk ɗaya kuke dan wlh ƙwara dabba dake Azmee,ita haka Allah ya halicce ta,Amma ke fa?mutunce wadda ta sani ta take sanin,ko yau kika faɗi kika mutu kinsan makomarki,babu ruwan Allah da ilimin da kike dashi,in har bakiyi aiki dashi ba,Toh ya tashi abanza don azabar da za'ayi maki ranar gobe ƙiyama tafi azabar da za'ayiwa kafiri,"

Lokaci guda Azmee ta juye tamkar ba ita ba,ta fito da ainihin suffarta ta mugaye marasa Imani,Idanuwanta sunyi jawur dasu wani kalar huci ke fita daga bakinta da hancinta,Kalaman Abu sun ƙona mata rai,Kamar ta shaƙo wuyanta haka take ji,

"Ki fita ki bani wuri Zainab!tunkafin Nayi maki Illa"

A harzuƙe abu tace"kiyi duk abunda kika ga dama Azmee,Wlh bazan ta6a karaya ba,koda kuwa zan rasa rayuwata saina tona maki asiri mushirika kawai,"abu nakai ƙarshen maganar,taja dogon tsoki ta juya a fusace tabar kitchen ɗin,

Komawa Azmee tayi saman ɗaya daga cikin kujerun dining na kitchen ɗin ta zauna,maganganun abu ta shiga tariyowa acikin kanta,tunda take a rayuwarta Wani ɗan adam bai ta6a fuskantarta ba,Ido cikin ido ya gaya mata baƙaƙen maganganu ba,in ba abu ba,Itace ta farko kuma ta ƙarshe don taci alwashin duk wanda yayi yunƙurin exposing ɗinta saita Kashe shi har LAHIRA,

Runtse idanuwanta tayi lokaci guda ta shiga tunanin Sehrish,sam bataso hakan ta faru da ita ba,ta ƙetare Iyakarta ne shiyasa Ta jefa ta a halin da take ciki,

Da sallama Omar ya shiga part din nashi,A lokacin Sgr yana ta Zarya acikin bedroom ɗin,lokaci bayan lokaci yakan juya ya kalli Sehrish dake kwance tana bacci,Ba ƙaramin jiki taji ba,don ma Allah Yasa ta samu emergency treatment a wurinshi,Da ba'a son me zai biyo baya ba,

Sam baiji sallamar da Omar yayi mashi ba,har saida ya Ambaci sunanshi"Rafayet"tukunna ya juyo tare da kallonshi,

Ƙarasawa wurinshi Omar yayi tare da dafa kafadarshi,

"Ya jikin nata"?

"tana samun sauƙi,nayi mata allurar bacci ne,in ba haka ba bazata daina firgitar da take yi ba,"

Ajiyar Zuciya Omar ya sauke tare da cewa"Allah ya bata lafiya,amma meke damunta ne?

"I don't even know,jira nake ta farka,Don in tambayeta,nasan zata faɗamun meke damunta,me take gani ne da yake razanar da ita,"

"Haka ya dace,ƴan uwanta na son ganinta,Zasu iya shigowa yanzu?"Omar yayi tambayar yana kallonshi,

Girgiza mashi kai yayi alamar a'a,sannan yace"sai dai zuwa anjima idan taji sauƙi,"

Omar yace"Okey,"harya juya zai fita ya kuma juyowa,

"Ya maganar Haroon"?

Sgr yace"Still bai farfaɗo ba,Nasan zuwa anjima zai tashi,"

Gyaɗa kai Omar yayi tare da juyawa ya fuce daga ɗakin,'

Wuraren Sallar Azhar gaba ɗaya suka tafi masallaci,Ya rage saura matan Acikin gidan,

Abu sam ta kasa samun natsuwa,gashi batasan ina aka kwantar da Sehrish ɗinba balle taje dubata,basu jima da kammala sallar Azhar ba,Abu ta mike tare da kallon Jahad"Inaso naga sehrish,gashi bansan inda aka kwantar da ita ba,

Jahad tace"Tana a ɗakin Ya rafayet,nima inason na ganta,"ta ƙarasa maganar tare da miƙewa,hosana ma ta miƙe"Nima zanje ganin rishi ɗin,"

Kowannansu sanye da hijabi,Atare suka nufi upstairs,Da sallama suka shiga falon babu kowa,kaitsaye suka wuce bedroom ɗinshi,daga ciki suka shiga,gwanin ban tausayi haka suka tsaya cirko cirko abakin gadon suna kallonta,Tana bacci tana firgita,Numfashinta na fita daƙyar daƙyar,

Zama Oummansu Tayi daga gefen gadon Yayin da su Jahad ke atsaye,idanuwansu cike tab da kwalla,

"Oumma wai meke damun rishi ne?duk tabi ta furgice ta fita hayyacinta,"

Hosana ce tayi maganar cikin shessheƙar kuka,

Abu tace"ku tayata da Addu'a in sha Allah zata samu sauƙi ne,"

Jahad tace"wlh dama ciwon ya dawo jikina,ita ta huta,Saboda taji jiki ba kaɗan ba,"

Hannu abu tasa tare da shafa fuskar Sehrish,aikuwa kamar jira take yi taji an ta6ata nan ta fara sambatu da muryarta da bata fita sosae saboda ciwon cikin bakinta tana faɗin"ku kira mun shi,dan Allah ku kira shi,Ya mu'allim nake son gani,"lokaci guda kuma tadaina sambatun

Kallon juna sukayi cike da mamaki,har suna haɗa baki wurin cewa"Ya mu'allim kuma?Wanene Shi"?

"Jiya tayi mun magana akanshi,Wai wani malaminsu ne Ya mu'allim,Ta sanar dani cewa Ya ta6a taimakonta,ko kunsanshi ne"?Tayi tambayar tana kallonsu jahad,

"Ni ko sunan ma banta6a ji ba,"acewar hosana,

Jahad tace"bazamu iya sanin malamin da take magana akai ba,tunda ba wurinmu ɗaya ba,"

Addu'a suka shiga yi suna tattofa mata ajikinta,basu bar ɗakin ba sai wuraren sallar La'asar,Suka tafi banda hosana,tana zaune gefenta,ta kasa ta tsare sai rishi ɗinsu ta farka,

Bayan sallar La'asar,Abusufyan tare da Abba Suka shigo cikin ɗakin,a bakin gadon suka tsaya suna kallonta,A lokacin hosana ta fita daga ɗakin

"Banji daɗi abunda ya faru ba,Allah Ya bata lafiya,"cike da jimami Abba yayi maganar,

Abusufyan yace"tabbas akwai abunda ke damunta,tana faɗin abunda mu bamu gani ba,kuma a sanadin hakan ta kusa lahanta kanta,In har bamuyi kokarin gano abunda ke damunta ba,za'a iya samun matsala,"yana kai ƙarshen maganar Abba yace"in sha Allah hakan ma bazata faru ba,Yanzu dai ita muke jira ta farka sai muji daga bakinta,Tayi mana bayanin abunda ke damunta,"

Sunjima suna tattaunawa,Anan su kanal Yousouf da sauran matasan gidan suka same su,Kowa ya shigo ɗakin sai ya yi ma Abusufyan ya jikin Sehrish,daga bisani bayan Sgr Ya dawo ne suka ɗan basu wuri,Ya jima yana jiran farkawar Sehrish Amma babu alamun baccin nata zai ƙare,

Wuraren karfe 8 na dare,Sgr da Omar suka nufi Medical room ɗinsu Wurin Haroon,Lokacin da suka shiga a kwance suka same shi yana ta faman Jan numfashi,Idanuwanshi sunyi jawur dasu jikinshi sai kerma yake yi,

Tsayawa Sgr yayi tare da goya hannayenshi saman ƙirjinshi,Omar kuma wuri ya samu gefen gadon Ya zauna yayin da idanuwanshi ke akan Haroon

"Ya jikin naka"?

Ba ƙaramin mamaki yayi ba,jin Omar yayi mashi ya jiki,yayi tsammanin da bugu zasu fara tambayarshi,

Daƙyar ya iya buɗe baki Yace"babu sauƙi,Naji jiki sosai,Rafayet baiyi mun da sauƙi ba jiyan nan,dan Allah Ya Omar ka taimaka mun nasan kafi shi sauƙin kai,wlh ni babu ruwana kashe Junaid da nayi ma kuskure ne,Sharrin shaiɗanne,In fact ni bayin kaina bane....."a fusace Sgr Ya daka mashi tsawa"Idan ka kuskura ka sake ambaton shaiɗan a wurin nan saina Canza maka kamanni,akwai wani shaiɗanin daya wuce kaine"?

Shiru yayi batare daya kuma cewa komai ba,Don bazai manta da lugudan wahalan daya shaba Adaren jiya,

A tsanake Omar ya soma magana"amsa ɗaya kawai nakeso a wurinka!Wanene yake baka Umarni?

"Wlh bazan Iya faɗa maku ba,Ae ko ban sanar daku ba,in har rafayet zai iya sanin duk wani abu da nake aikatawa,Sanin wanda ke bani Umarni bazai gagare shi ba,Yasan Komai"

Haushi kamar ya shaqe shi haka yake ji,daƙyar ma yake magana saboda raɗaɗin ciwon da yake ji,Ga Yunwar da yake ji,ba don Omar ya hanashi Dukanshi ba,da ba abunda zai hana ya karairaya ƙasusuwan Jikinshi,ya tsani haroon kamar mutuwarshi,

"Rafayet baisan komai ba,kai nakeso ka sanar dani!Haroon ka amsa mun tambayata,kai da Uban wanene kuke aika aika acikin gidan nan?"

Shiru haroon yayi,A hasale Sgr ya ɗaga Hannu zai mauje mashi kai,Omar yayi saurin ruƙoshi,"just leave him,Idan bai amsa mana ba,Wayar shi zata bamu amsa,"

Basu bar ɗakin ba sai da suka ɗaure haroon jikin gadon sosai,Suka rufe bakinshi,Yarda baza aji Sambatun shi ba"

Datse ƙopar ɗakin Sgr Yayi,Sun jima suna tattaunawa da Omar kafin Ya wuce upstairs,Omar kuma ya nufi sashen su Abbansu,

Lokacin daya shiga bedroom ɗin,Still Sehrish bata farka ba,toilet Ya shiga,After some minutes ya fito sanye da bathrobe da alama wanka yayi,gaban mirror ɗinshi Ya tsaya yana kallon kanshi ta mirror,Abubuwa dayawa suna yi mashi yawo akanshi,yanzu baida burin daya wuce ya kawo ƙarshen maƙiyansu cikin kwanakin nan,da zarar ya gama dasu Zai fara tunanin komawa U.S,

Yana cikin zancen zucin nan,Ya fara Jin numfashin Sehrish dake fita da ƙarfi da ƙarfi,Da sauri Ya koma gefen gadon Ya zauna yana kallonta,A hankali ta soma ƙoƙarin buɗe idanuwanta masu ɗauke da bacci,biji biji ta fara ganinshi,har sai da ta sanya hannunta saman fuskarta tana mutsustsuka idanuwan tukunna ta samu damar ganin shi da kyau,kwata kwata Jikinta babu ƙwari daƙyar ta samu ta miƙe zaune,Ciwo na yini ɗaya amma duk ta rame,idanuwanta duk sun faɗa,lips dinta sun dan kumbura,jikinta sai kerma yake Yi,

"How was ur body"?yayi tambayar Yana kallon Clavicle ɗinta,

Shuru bata bashi amsa ba,Sai dai zuba mashi ido da tayi tana kallonshi,Sake maimaita mata yayi"Ya jikin naki,"nan ma shiru bata bashi amsa ba,Cike da mamaki yace"Baki ji ina magana ba"

Tunawa da ciwon bakinta ne yasa shi yin shiru,don yasan bazata iya magana ba sai a hankali,

"If u can't talk to me,zaki iya yi mun alama ta yarda zan fahimci abunda ke damunki,"

Lumshe idanuwanta tayi tare da buɗesu a hankali

"Are u hungry"?.

Da sauri ta girgiza mashi kai alamar a'a,ba don taso ba,ita kaɗai tasan halin da take ciki,Ga matsiyaciyar yunwa tana ji amma fargabar abunda zata ƙara gani acikin abincinta take ji,

Moving yayi kusa da ita,tare da sanya tafin hannunshi ya ruƙo kanta,A saman ƙirjinshi ya kwantar da ita,nan take taji natsuwa ta zo mata,hawaye ne suka soma zarya akan fuskarta,taso ace zata iya buɗe baki ta sanar dashi ainihin abunda ke damunta amma ta kasa,harshenta Ya raunata sosai,magana ma wuya take yi mata,

Shafa sumar kanta ya soma yi har izuwa tsakiyar bayanta,sosai ta manne mashi tana shaƙar kamshin jikinshi,

"I really worried about it,pls Tell me what scared you?meyasa kike firgita"?

Yayi maganar tare da mayar da hannunshi saitin zuciyarta dake ta bugawa da ƙarfi da ƙarfi,tunda ya aza hannun kuma sai heartbeat ɗin nata ya dai daita,

Ƙanƙameshi tayi sosai,tana ji aranta kamar bazata rayu ba,tun da ta fara wannan ƴan gane ganen na tashin hankali,

Waist ɗinta Ya ruƙo tare da Janyeta daga jikinshi,Miƙa hannunshi yayi gaban drawer chest,Ya curo biro tare da jotter,

Miƙa mata yayi tasa hannu biyu ta kar6a

"Ki rubutamun duk wani abu dake damunki anan,"

Hannunta na kerma ta buɗe empty page ta soma rubutu,bayan ta kammala ta miƙa mashi jotter ɗin

Hannu yasa ya kar6a yana karantawa

_Oumma tasan komai,Ka tambayeta zata faɗa maka abunda ke damuna_

Wannan shi ne abunda Sehrish ta rubuta mashi,

ɗagowa yayi tare da kallonta suka haɗa ido,hannu ya zura cikin front pocket ɗinsa Ya zaro wayarshi,Nan take ya kira Fawan ya sanar dashi cewa Ya kira Mashi Oummansu,

Miƙewa Yayi ya nufi cikin ɗakin,sai gashi ya dawo sanye da sleeping dress ɗinshi riga da wando Maroon colour,Gefen gadon Ya koma ya zauna yana jiran zuwan Abu,

Kusan 15 mins,Abu tayi sallama a ƙopar ɗakin,

"Assalamu alaikum,"

"Wa'alaikum salam,"ya amsa mata tare da bata izinin shiga daga ciki,

Tana sanye da hijab ajikinta,Tunkan ta ƙarasa Sgr ya mike tare da janyo mata chair ɗin dake gaban dressing mirror ɗinshi ya ajiye mata ita,Tunda ta shigo ɗakin idonta ke akan Sehrish,Ba ƙaramin daɗi taji ba da sehrish ta farka,da alama jikin nata da sauki duk da akwai sauran ciwo atattare da ita,

"Ya jikin naki"?tayi tambayar bayan ta zauna,shiru Sehrish bata ce uffan ba,Hakan yasa ta ɗan tashi hankalinta,

"Kada ki damu,ba zata iya magana a yanzu ba,saboda raunin dake abakinta,

Ajiyar zuciya abu ta sauke kafin tace"Allah ya baki lafiya,"

"Ameen"ya amsa mata amadadin Sehrish ɗin,don ita sai dai ta ɗaga kai,

gaisar da ita Sgr yayi cikin girmamawa,ta amsa mashi fuskarta asake,

"Inaso ki faɗamun meke damunta ne"?

Buɗe baki abu tayi zata yi magana kenan taji anshaƙe mata maƙoshinta,runtse idanuwanta tayi tana ambaton Sunan Allah acikin Zuciyarta,

"Be calm and answer me pls"Ya faɗi hakan ne don Ya lura tamkar bata a cikin natsuwarta,Sehrish kuwa hankalinta ya tashi ganin Oummansu ta kasa buɗe baki tayi magana,tuni idanuwanta sun cicciko da ƙwalla,

Wasu addu'oi abu ta shiga jerowa acikin bakinta,da ƙarfi da ƙarfi,bata daina ba har sai da Maƙoshinta Ya buɗe,nan take zufa ta wanke mata fuskarta,miƙewa Sgr yayi cikin sauri ya shiga palour,within secs ya dawo hannunshi ɗauke da bottle water,zama yayi tare da cire murfin ya miƙa ma Abu,hannu biyu tasa ta kar6a,kusan rabin ruwan ta shanye,janye robar tayi daga bakinta,har lokacin tana cigaba da karanto addu'o'in neman tsari a wurin ubangiji don ta gane cewa so ake a hanata magana,gashi ita kuma gwana ce wurin yin ibada, da kuma yin azkhar da sauransu,zaiyi wuya sihiri ya kama irinsu wani lokacin sai dai suci wahala,

Lokacin da taji zata iya magana,da sauri ta soma bayyana mashi halin da sehrish ke ciki"tun jiya da ta shiga ɗakin Azmee bata ƙara samun natsuwa ba,ta sanar dani cewa tana ƴan gane gane,wasu abubuwa nayi mata gizau,kamar ɗazu da safe lokacin da muke cin abinci,Sehrish ta dinga sambatu tana faɗin tsutsotsi ne acikin plate ɗinta,har tayi wurgi da plate ɗin ta watsa da gudu ta shiga ɗaki,wannan ne silar data rikice ta shige toilet tana wanke bakinta da Omo da soso,kamar yarda ka gani....."

Dakatawa ta ɗan yi da yin maganar tana faman sauke ajiyar zuciya,Sehrish sai murmushi take yi farin ciki kamar ta miƙe ta rungume Oummansu,

Shiru Sgr yayi yana kallonta yayin da yake nazarin wani abu acikin brain dinshi,bakomai ya faɗo mashi arai ba face daren jiya da Sehrish tazo ɗakinshi ta tsorata harta yi wurgi da plate ɗin hannunta,tana fadin Ya rafayet maciji kunama zasu harbeka,anan ya gane cewa Bayan ta fito daga ɗakin Azmee ne ta shigo ɗakinshi,

Jinjina kanshi ya ɗan yi tare da cewa"Kina Zargin Azmee"?

Da sauri abu ta ɗaga mashi kai Alamar eh,

"Meyasa kike zarginta"?

"Saboda na santa,lokacin dana haifi su Sehrish,Itace Ƴar uwar sayyadi wadda tazo yi mun wankan jego,"

Tunkan takai ƙarshen maganar Sgr yace"Kenan ita ƴar uwar shi ce?",

Jinjina mashi kai tayi alamar eh,murmushin takaici Sgr ya saki,

Yana ƙoƙarin buɗe baki ya kuma tambayarta,Yaji Sehrish ta ruƙo hannunshi,da sauri yakai idonshi wurinta,

Da hannu ta dinga yi mashi Alamar ya miƙo mata jotter dinnan zata yi rubutu,

Hannu yasa ya dauki jotter ɗin tare da mika mata,dama biron na hannunta,

Zane yaga tana yi maimakon rubutu bayan ta kammala ta mika mashi jotter ɗin,

Hannu yasa ya kar6a tare da kallon abunda ta zana,Zobe ne ta zana,bai gane me take nufi ba,

"Zan iya ganin me ta rubuta?"abu ce tayi tambayar,

Miƙa mata jotter din

Yayi tasa hannu ta kar6a,koda abu taga zanen sai ta tuna da binciken da Sehrish ke yi dangane da Junaid,dayake ta bata labarin mutuwarshi,baiwar Allah tana so tayi mashi maganar Junaid ɗin ta kasa,Gashi ita kuma abun ta manta bata sanar dashi ba,

"Kin gane me take nufi"?

Jinjina kai abu tayi kafin ta ɗaura da bayani"Ta sanar dani komai daya faru dangane da mutuwar ƙaninku Junaid!"tunda sgr yaji ta ambaci junaid,hankalinshi gaba ɗaya ya koma kanta,

"Akwai wata rana da ta shiga ɗakin Azmee,zatayi sallah tana ƙoƙarin ɗauko hijabi acikin wardrobe ɗin ita azmeen,Sai ga zoben ƙaninku na Diamond ya faɗo daga cikin wardrobe ɗin,A binciken da sehrish tayi ta gano cewa tare da zoben nan Shi Yaron ya fita aranar da al'amarin ya faru kuma abun mamaki Zoben nan nashi baiyi komai ba!babu alamar wuta taci shi!"

Gaban Sgr ne ya faɗi rasss!ya ware idanuwanshi gaba ɗayansu,Abun ba ƙaramin girgiza shi Yayi ba,jikinshi har kerma yake yi,aruɗe yace"Taya akai Ita reesh ɗin tasan cewa tare da zoben Ya fita aranar'?

"Ta hanyar hotunan da suka ɗauka tare da Junaid a wayar Jahad,"

A hanzarce Sgr ya ɗauki wayarshi tare da dannawa Fawan kira,tana fara ringing ya ɗaga kiran,

"Fawan Am sorry na takura ka ko"?

On ther hand fawan yace"A'a babban Yaya,baka takuramin ba,"

"Idan kana kusa,pls inaso ka kira mun Jahad,ka sanar da ita cewa tazo mun tare da wayarta da kuma wayar Sehrish ina buƙatar ganinsu,"

"Toh babban Yaya"yana kai ƙarshen maganar ya ajiye wayar,zuciyarshi sai faman tafarfasa take yi,ita kanta daurewa kawai takeyi saboda maƙoshinta da ake ƙoƙarin shaƙewa ta dage sai ta faɗi gaskiya,koda kuwa Rai zaiyi halinsa,

Bayan wasu mintuna,Jahad ta faɗo ɗakin da sallama a bakinta,jikinta sanye da dogon hijabi,yayin da hannunta ke ruƙe da wayarta da kuma wayar sehrish,

Atare suka amsa mata sallamar,shiga cikin ɗakin tayi,gaba daya idanuwanta na akan Sehrish zaune tana ta murmushi,wani irin farin ciki ne ya lullu6e Jahad,

"Sehrish Ya jikin naki?na damu sosai akan halin da kika shiga"

"Jahad Rishi bazata iya magana ba a yanzu,ki tayata da addu'a,"acewar Oummansu,

Jikin Jahad ba ƙaramin sanyi yayi ba,miƙa mashi wayoyin tayi,Yasa hannu ya kar6a,danna wayar Jahad ya shiga yi,direct ya shiga Gallery ɗinta,

ɗagowa yayi tare da kallon Jahad"Ina hotunan da kukayi keda junaid aranar da kuka fita shan ice cream"?

"Suna acikin Gallery ɗina,daga ka shiga zaka gansu,"

"I did not see anything,ko kin gogesu ne"?

Gaban abu ne ya faɗi rass,Ita kanta Sehrish saida hankalinta ya tashi,

Jahad tace"Wlh ya rafayet ban gogesu ba suna acikin wayata,ko yanzu haka kafin nazo nan hotunan nake kallo"

Miƙa mata wayar yayi"nuna mun su,"

Bayan Jahad ta kar6i wayar,ta shiga neman pictures ɗin gaba ɗaya an goge mata su har vedios din daga cikin wayarta,

Tamkar zata fashe da kuka,"Ya rafayet wlh an goge munsu,bansan ya akai ba,"

"Wani ya amsa wayarki ne"?

Girgiza kai tayi"a'a,duk yinin yau wayata tana a hannu na,"

Mayar da idanuwanshi yayi kan abu"taya zan gane cewa,Junaid ya fita da zoben a hannunshi?ina yin amfani da shaida ne,kafin na yanke hukunci,"

Gaba ɗaya sunyi shiru,jikin kowa yayi la'asar musamman Sehrish domin kuwa harta fara zubar da kwalla,Azmee tayi masu tsiya suna ƙoƙarin fallasa ta ita kuma ta hana hakan,Shi kuma Sgr bai yarda da sihiri ba,koda zasu fada mashi cewa tana amfani da sihiri zaiyi wuya ya yarda,

Hannu Sehrish tasa tare da ta6o shi,juyawa Sgr yayi yana kallonta,Nuna mashi wayarta tayi da yatsanta alamar tana buƙatarta,

Miƙa mata wayar yayi,tasa hannu ta kar6a,

Tana kunna Power din wayar ta kawo haske,Sai ga text message Ya shigo ta layin AMRISH!

Yaushe rabon da ta samu layin Amrish harta manta,kullum in ta kira kashe take samun wayar,Yanzu haka da ta kar6i wayar Amrish take so Ta tura ma saƙo akan ta nemo mata number Ya mu'allim ɗinsu,

Shiga message ɗin tayi,ta ƙura ido tana kallon jagwalgwalon Rubutun da aka turo mata,Na haruffan da aka cakuɗesu,abun ya ɗaure mata kai!Nikaina Boss Ya ɗaure mun kai!

Abban Sojoji Takun Karshe Book 3 Chapter 110 (2024)
Top Articles
Latest Posts
Article information

Author: Mrs. Angelic Larkin

Last Updated:

Views: 5853

Rating: 4.7 / 5 (67 voted)

Reviews: 90% of readers found this page helpful

Author information

Name: Mrs. Angelic Larkin

Birthday: 1992-06-28

Address: Apt. 413 8275 Mueller Overpass, South Magnolia, IA 99527-6023

Phone: +6824704719725

Job: District Real-Estate Facilitator

Hobby: Letterboxing, Vacation, Poi, Homebrewing, Mountain biking, Slacklining, Cabaret

Introduction: My name is Mrs. Angelic Larkin, I am a cute, charming, funny, determined, inexpensive, joyous, cheerful person who loves writing and wants to share my knowledge and understanding with you.